Asalin hoton, Getty Images
- Marubuci, Abdullahi Bello Diginza
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Abuja
- Twitter,
- Aiko rahoto daga Abuja
Wannan maƙala ce da ta yi waiwaiye kan muhimman batutuwan da suka faru a Najeriya da makwabciyarta Jamhuriyar Nijar a cikin shekarar 2023
Yayin da shekarar 2023, ke tattara komatsanta don yin ban-kwana, tarihin Najeriya da Nijar ba zai taɓa cika ba sai da shekarar.
Abubuwa da dama sun faru a waɗannan ƙasashe, waɗanda tarihi ba zai taɓa mantawa da su ba.
Manyan abubuwan da suka faru a Najeriya
An samu faruwar al’amura da dama a Najeriya cikin shekarar ta 2023, kama da gada siyasa da tatalin arziki da tsaro da sauran fannoni.
Babban zaɓen 2023
Asalin hoton, Getty Images
A ranar 25 ga watan Fabrairu ne aka gudanar da babban zaɓen ƙasar
A Najeriya an buɗe shekarar 2023 ne da shirye-shiryen babban zaɓen ƙasar, wanda aka shafe kusan shekara guda ana shirya masa.
A ranar 25 ga watan Fabrairu ne aka gudana da zaɓen shugaban ƙasar, zaɓen da ya ja hankali duniya, saboda matsayin ƙasar da ke yi wa kallo a matsayin giwar Nahiyar Afirka.
A ranar 28 ga watan Fabrairun ne shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya sanar da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ƙuri’a miliyan 8,794,726.
Babban abokin hamayyarsa a zaɓen tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar na jamiyyar PDP ya samu ƙuri’a miliyan 6,984,520.
Sai kuma dan takarar jam’iyyar LP, Peter Obi wanda ya samu ƙuri’a miliyan 6,101,533.
Yayin da tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zo na huɗu da ƙuri’a miliyan 1,496,687.
Zaɓen da manyan ‘yan takarar Adawa biyu Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP suka yi watsi da sakamakon, inda suka garzaya kotu don ƙalubalantarsa.
Sai dai a ranar 26 ga watan Octoba kotun ƙolin ƙasar ta koriu ƙarar tasu tare da tabbatar da nasarar shugaba Tinubu a matsayin halastaccen shugaban ƙasar.
Baya ga zaɓen shugaban ƙasar an kuma gudanar da zaɓen gwamnoni a jihohin ƙasar da dama ranar 18 ga watan Maris, sai kuma wasu da aka gudanar ranar 11 ga watan Nuwamba.
Canjin gwamnati
Asalin hoton, Getty Images
Gudanar da babban zaɓe na nufin sauyi a jagorancin gwamnati, a ranar 29 ga watan Mayu ne kuma sabon shugaban Bola Tinubu ya karɓi ragamar mulkin ƙasar daga hannun tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari, wanda ya shafe shekara takwas yana jan ragamar ƙasar.
Haka kuma batun yake a sauran jihohin ƙasar, inda aka gudanar da zaɓen gwamnan, nan ma an samu sauyin gwamnati a wasu jihohin, yayin da wasu kuma gwamnanonin da ke kan mulki suka ci gaba da jaroncin jihohin a wa’adin mulki na biyu.
Haka batun yake a majalisun dokokin ƙasar, da na jihohi, inda a nan ma aka samu sauyi ta fuskar zubin majalisun da kuma jagororin majalisun.
Majalisar dattawan ƙasar ta zaɓi Godswill Akpabio a matsayin sabon shugaban majalisar ta 10, yayin da Honarabul Tajudeen Abbas ya kasance sabon kakakin majalisar wakilan ƙasar.
An gudanar da bikin naɗin ministoci cikin watan Agusta
Haka batun yake a majalisar zartarwar ƙasar, inda cikin watan Agusta aka rantsar da sabbin ministocin gwamnatin da za su taimaka wa ɓangaren zartarwa wajen gudanar da ayyukan gwamnati.
Ministocin sun ƙunshi tsofaffin gwamnoni da masana a fannoni daban-daban.
Cire tallafin man fetur
Asalin hoton, Getty Images
A jawabinsa na farko bayan rantsar da shi a matsayin sabon shugaban ƙasar ranar 29 ga watan Mayu, shugaba Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur da ƙasar ta jima tana zuba maƙudan kuɗi a ɓangaren domin sauƙaka wa ‘yan ƙasar.
Wannan mataki ya haifar da tashin farashin man feturm inda farshin ya ninka fiye da sau uku, sannan sauran abubuwa cikin har da kayayyakin masarufi da na sufuri suma suka tashi.
Wani abu da ya jefa ‘yan ƙasar dama cikin wahalhalun matsin tattalin arziki.
Lamarin da ya sa ƙungiyoyin ƙwadogon ƙasar gudanar da jerin zanga-zanga tare da barazanar shiga aikin aiki, matsawar ba a mayar da tallafin ba.
Saukewa da kama gwamnan CBN da shugaban EFCC
Asalin hoton, Getty Images/BBC
Tsohon gwamnan CBN da tsohon shugaban EFCC
Daga nan ne kuma hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta kame shugabannin hukumomin biyu tare da tsare su a hannunta har na tsawon lokaci, inda daga baya lauyoyinsu suka garzaya kotunan ƙasar don neman sakinsu.
Daga ƙarshe dai tsohon shugaban na EFCC AbdulRasheed Bawa ya samu beli, inda aka sake shi ya koma gida, yayin da shi kuma tsohon gwamnan na CBN har yanzu ke tsare a gidan yarin Kuje, bayan gaza cika sharudan beli.
Naɗa manyan hafsohin tsaro
Asalin hoton, NTA
Wani abin mamaki game da naɗin sabbin hafsoshin tsaron shi ne yadda shugaba Tinubu ya zaƙulo hafsoshin da ke da ƙananan muƙamai don ba su muƙaman shugabantar rundunonin tsaron ƙasar.
Kasancewar akwai manyan janar-janar fiye da 100 da ke gabansu a muƙamai, amma duk da haka shugaban ya dauko su don yi musu wannan matsayin.
Dama dai al’ada ce a aikin soja, idan aka nada na kasa a matsayin shugaba na saman su ajiye aiki, don ana fargabar watakila ba za su iya karbar oda daga wajensa ba.
Sannan kuma ya sanar da naɗin Mallam Nuhu Ribadu a matsayin mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro.
Batun Ministan El-Rufai da Wike da Maryam Shetti
Asalin hoton, FACEBOOK/NASIR EL-RUFAI
Bayan tantance El-Rufai, daga ƙarshe majalisa ba ta tabbatar da shi ba
Sunayen sun ƙunshin na tsoffin gwamnoni da masana daban-daban.
Sai dai wani babban abu da ya ja hankali game da sunayen shi ne ganin sunan tsohon gwamnan Ribas Nyesom Wike a ciki, kasancewarsa ɗan jam’iyyar adawa ta PDP, wani abu da ba a saba gani ba a ƙasar, a samu ɗan jam’iyyar adawa a ƙungin majalisar zartarwa.
Haka kuma bayan rukunin farko na sunayen ministocin da Tinubu ya aike, ya sake aike wa majalisar wasu kunshin sunayen ranar 2 ga watan Agusta, ciki har da sunan Dakta Maryam Shetti, matashiyar ‘yar siyasa daga jihar Kano.
Asalin hoton, Maryam Shetti/Facebook
Batun matashiyar ‘yar siyasar ya ja hankali sosai a ƙasar
To sai dai bayan da ta halarci majalisar domin tantacewa, sai kwatsam shugaban kasar ya sanar da janye sunanta daga cikin jerin sunayen, tare da maye gurbinta da Dakta Mariya Bunkure daga jihar.
Wannan batu ya haifar da ce-ce-ku-ce a kasar, domin kuwa al’amari ne da ba a saba gani ba a kasar.
Shugaban Majalisa Godswill Akpabio ya ce majalisar na jiran rahoton jami’an tsaro kafin su tabbatar da mutanen uku.
Da haka ne kuma maganar ta sha ruwa domin ba su samu shiga majalisar ministocin ba.
Harin Tudun Biri
Asalin hoton, NIGERIAN AIRFORCE
Hari kan masu maulidi ya ƙauyen Tudun Biri ya yi matuƙar tayar da hankali a ƙasar
Kauyen Tudun Biri ya shiga kanun labarai a shekarar 2023, bayan da jirgin sojin Najeriya ya yi kuskuren kan hari kan masu maulidi a kauyen da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.
A ranar 3 ga watan Disamba ne jirgin sojin maras matuƙi ya yi kuskuren jefa boma-bomai har guda biyu kan fararen hular, lamarin da ya yi sanadiyyar kisan aƙalla mutum 85, tare da jikkata wasu da dama.
Wannan batu ya ja hankalin ‘yan ƙasar da dama, inda gwamnatin tarayya ta yi alkawarin gudanar da bincike tare da hukunta duk waɗanda aka samu da hannu a lamarin.
Haka kuma gwamnatin ta amince da biyan diyyar mutanen da suka mutu, tare da alƙawarta gina wa mazauna ƙauyen ababen more rayuwa da suka hadar da asibiti da titi da makaranta.
Rububin shiga kundin bajinta na Guiness
Asalin hoton, Hilda Bachi/X
Hilda Baci ta zama zakaran gwajin dafi bayan ta kafa tarihin girki a watan Mayu
Wani abu da ba za a manta da shi ba a Najeriya game da shekarar 2023 shi ne batun rububin kafa tarihi.
An samu matasa masu yawan gaske da suka yi yunurin shiga kundin bajinta na duniya wato ‘Guinness World Records’ da ake adana abubuwan bajinta, na duniya.
A cikin watan Mayu ne Hilda Baci ta ɗora tukwane a murhu ta shiga girke-girke babu ƙaƙƙautawa don ta kafa tarihi.
Inda ta samu nasarar kafa tarihin daɗewa taa girki bayan shafe sa’o’i 93 tana girki kamar yadda kunfin ya tabbatar.
Daga nan ne kuma ‘yan ƙasar suka riƙa rububin kwaikwayarta, ciki har da wadda ta yi yunƙurin kafa tarihin daɗewa tana wanki, lamarin da ya sa ta ƙare a asibiti.
Manyan abubuwan da suka faru a Nijar
Asalin hoton, AFP
Shugaban mulkin sojin Nijar
Juyin mulki
Babban abin da za a fi tuna shekarar 2023 a jamhuriyar Nijar shi ne batun juyin mulki da sojoji suka yi wa zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.
A ranar 26 ga watan Yuli ne sojojin Nijar suka sanar da yi wa Bazoum juyin mulki bayan da tun farko suka tsare tsare da hani shi fitowa a gidansa da ke fadar gwamnati ƙasar.
Janar Abdurrahamane Tchiani, wanda shi ne babban kwamandan dakarun tsaron fadar shugaban kasar ne ya jagorancin kifar da gwamnatin, wanda kuma daga baya aka ayyana shi a matsayin sabo shugaban mulkin sojin ƙasar.
Wannan mataki ya haifar da ce-ce-ce-ku tare da yin Allah wadai daga ƙungiyoyi da ƙasashe da dama ciki har da ƙasashen Yamma, musamman Amurka da Faransa.
Sojojin dai sun ci gaba da tare shugaba Bazoum tare da matasar da kuma ɗansa a fadar gwamnati, bayan da suka naɗa ministoci domin ci gaba da gudanar da gwamnati.
Ƙaƙaba wa ƙasar takunkumai
Asalin hoton, Ecowas
Bayan juyin mulkin ne kuma ƙungiyar raya tata;in arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta nuna adawarta da shi, inda ta gargaɗi sojojin da su gaggauta mayar da Bazaoum kan karagar mulki, matakin da sojojin suka yi twatsi da shi.
Daga nan ne kuma kungiyar ta yanke shawarar ƙaƙaba wa ƙasar jerin takunkuman karya tattalin arzikin da nufin tilasta wa sojoin mayar da mulki ga Shugaba Bazoum.
Wannan mataki ya yi matuƙar tasiri wajen jefa ‘yan ƙasar cikin matsain tatalin arziki, sakamakon tashin farashin kayayyaki a ƙasar.
Ziyarar manyan mutane don sasantawa
Asalin hoton, EL HAJ
Tawagar malamai daga Najeriya sun sha ziyarce-ziyarce Nijar domin sasantawa
Bayan juyin mulkin ne dai wasu manyan mutane musamman daga Najeriya suka riƙa kai ziyara Nijar domin sasantawa tsakani sojojin da ƙungiyar Ecowas.
Daga ciki akwai tawagar manyan malaman addini na Najeriya ƙarƙashin jagorancin Sheikh Abdullahi Bala Lau suka riƙa zariya da nufin samun daidaito tsakanin Ecowas da sojojin da suka yi juyin mulki a ƙasar.
Haka kuma an samu tawagar wakilan Ecowas karƙashin jagorancin tsohon shugaban Najeriya Janar Abdulsalami Abubakar da Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammad Sa’ad Abubakar Abubakar lll.
Sannan kuma shi ma Khalifan Tijjaniya, wato sarkin Akno na 14 Muhammadu Sanusi ll, wanda shi ma ya ziyarci ƙasar da nufin duk dai domin sansantawa.
Asalin hoton, Muhammadu Sanusi II
Sarkin Kano na 14 na daga cikin manyan mutanen da suka shiga tsakani
Korar sojojin Faransa
Bayan juyin mulkin ne kuma sojojin mulkin na Nijar suka sanar da korar dakarun faranmsa da ke ƙasar, bayan sanar da yanke duk wata hulda tsakanin ƙasar da tsohuwar gijiyar tata
Sojojn na Nijar sun zargi Faransa da kai wani mummunan hari kan jami’an tsaron ƙasar a Bourke Boukey a yankin Dargol da ke jihar Tillabery, lamarin nda ya yi sanadin mutuwar dakarun ƙasar da dama.
Wata sanarwa da sojojin ƙasar suka fitar na cewa sojojin Faransar ne suka kai harin, inda suka kuɓutar da wasu da suka kira yan ta’adda 16 tare da kashe mata sojojin da yanzu haka ba su san adadinsu ba.
Ƙulla sabon ƙawancen Sahel
Asalin hoton, Reuters
Haka kuma acikin watan Disamba ne Jamhuriyar ta Nijar ta sanar da ficewa daga ƙawancen kungiyar G-5 Sahel mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, tare da kafa wani sabon kawancen soji tare da ƙasashen Mali da Burkina Faso.
Ƙasashen uku wadanda dukakkansu ke ƙarƙashin mulkin soji, sun kafa ƙungiyar ne da nufin kare taimaka wa tare da kare kansu daga barazanar hari daga wata ƙasa ko ƙungiya daga wajen ƙasar.
Duka ƙasashen uku dai na fuskantar matsi daga ƙungiyar Ecowas bayan juyin mulkin soji da aka yi a ƙasashen.
Neman ƙulla ƙawance da Rasha
Tun bayan juyin mulki ne kuma al’ummar ƙasar da sojojin ke ta kiraye-kiraye ga ƙasar Rasha da ta zo domin kulla abon ƙawance da ita.
A cikin watan Disamba ne kuma wakilan gwamnatin Rashar suka ziyarci Jamhuriyar Nijar, inda suka gana da shugabannin mulkin soji ƙasar.
Wani mataki da masana tsaro ke kallo a matsayin yunƙurin Rashar na amincewa da bukatar ƙasar na ƙulla ƙawance da ita.