“APC na amfani da bangaren shari’a domin murkushe jam’iyyun hamayya”

0
13


Atiku Abubakar

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Atiku Abubakar

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya wuce , Atiku Abubakar ya yi zargin cewa jam`iyyar APC mai mulki na amfani da bangaren shari`a da nufin murkushe jam’iyyun hamayya.

Tsohon mataimakin shugaban kasa ya yi misali da hukuncin da kotunan daukaka kara suka a yanke a wasu jihohi, ciki har da Zamfara da Filato da Kano da Nasarawa, yana cewa gwamnati na rabewa ne da shari`a wajen kwace jihohin da ke karkashin ikon jam’iyyun adawa.

Sai dai jam’iyyar APC ta musanta zargin

Atiku Abubakar ya ce sun lura da take-taken jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, kuma sun fahinci cewa da sannu tana nema ta murkushe hamayya baki daya.



Source link

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here