- Rabiu Kwankwaso, jagoran jam’iyyar NNPP, ya taya kungiyar kwallon kafa ta Najeriya (Super Eagles) murnar lallasa kasar Guinea-Bissau
- Wannan nasarar da Super Eagles suka samu akan Guinea-Bissau ya ba su damar zuwa wasannin zagaye na 16 a gasar AFCON2023
- Kwankwaso ya karfafawa kungiyar guiwa tare da fatan za su ci gaba da samun nasara a wasannin su na gaba don lashe gasar kofin
Sani Hamza, kwararren edita ne a fanni n nishadi, al’amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Jigon jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso ya taya kungiyar kwallon kafa ta Najeriya (Super Eagles) murnar zuwa zagaye na gaba a gasar cin kofin Nahiyar Afirka (AFCON2023).
Kwankwaso ya ce kokarin da kungiyar Super Eagles ta yi na zuwa zagaye na gaba abin a yaba ne matuka.
![](https://i0.wp.com/netstorage-legit.akamaized.net/images/3ccc97a825fb4cbe.png?w=696&ssl=1)
Kara karanta wannan
20217: Tsohon hadimin Buhari ya bayyana abun da dinkewar Kwankwaso da Ganduje ke nufi ga PDP
![Kwankwaso ya jinjinawa SuperEagles Kwankwaso ya jinjinawa SuperEagles](https://i0.wp.com/netstorage-legit.akamaized.net/images/199623a82b5baa91.jpg?resize=696%2C348&ssl=1)
Hoto: @KwankwasoRM, @NGSuperEagles
Asali: Twitter
Yadda tawagar Najeriya ta fafata zuwa mataki na gaba
A ranar Litinin, Super Eagles ta lallasa kungiyar kwallon kafa Guinea-Bissau da ci daya mai ban haushi, a wasan karshe na rukunin A wanda ya ba ta damar zuwa wasan zagaye na 16.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kungiyar wacce ke karkashin mai horo Jose Peseiro ta kara da Guinea-Bissau ne bayan fafatawa da kasar Ivory Coast wacce ita ma ta lallasa ta da ci daya mai ban haushi, rahoton Channels TV.
Duk da cewa sun sha matsin lamba a zagayen wasan na farko, sun dawo da karfinsu bayan zuwa hutu, inda dan wasan Guinea-Bissau ya zura kwallo a gidansu a kokari cire ta.
Sakon da Kwankwaso ya aika wa Super Eagles
A halin yanzu dai, Super Eagles za su ci gaba da zama a birnin Abidjan domin karawa ranar Asabar da kungiyar da za ta ci wasan rukunin C, tsakanin Senegal, Guinea ko Kamaru.
![](https://i0.wp.com/netstorage-legit.akamaized.net/images/125fd0fe4fe61f8f.jpg?w=696&ssl=1)
Kara karanta wannan
Ba Za Ta Yiwu ba: Dattawan Arewa Sun Yi Tir da Dauke Manyan Ofisoshi Daga Abuja Zuwa Legas
Rabiu Kwankwaso sakon taya murnar da ya aika wa Super Eagles a shafinsa na Twitter ya ce:
“Kun cancanci yabo na tsallakawa zuwa zagaye na gaba. Ku kara kokari don samun nasara a wasannin ku na gaba.”
Karanta sakon a nan kasa:
Karatu da haddar Al-Kur’ani na gyara kwakwalwa – Gwamna AbdulRazaq
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya ba al’ummar Musulmi musamman matasa shawarar mayar da hankali wajen karatu da haddar Al-Kur’ani mai girma.
A cewar Gwamna AbdulRazaq, haddar littafin mai tsarki na gyarawa tare da saita kwakwalwar mai karanta shi.
Asali: Legit.ng