AFCON: Kwankwaso Ya Taya Tawagar Najeriya Nasarar Hayewa Mataki Na Gaba

0
6


  • Rabiu Kwankwaso, jagoran jam’iyyar NNPP, ya taya kungiyar kwallon kafa ta Najeriya (Super Eagles) murnar lallasa kasar Guinea-Bissau
  • Wannan nasarar da Super Eagles suka samu akan Guinea-Bissau ya ba su damar zuwa wasannin zagaye na 16 a gasar AFCON2023
  • Kwankwaso ya karfafawa kungiyar guiwa tare da fatan za su ci gaba da samun nasara a wasannin su na gaba don lashe gasar kofin

Sani Hamza, kwararren edita ne a fanni n nishadi, al’amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Jigon jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso ya taya kungiyar kwallon kafa ta Najeriya (Super Eagles) murnar zuwa zagaye na gaba a gasar cin kofin Nahiyar Afirka (AFCON2023).

Kwankwaso ya ce kokarin da kungiyar Super Eagles ta yi na zuwa zagaye na gaba abin a yaba ne matuka.

Kara karanta wannan

20217: Tsohon hadimin Buhari ya bayyana abun da dinkewar Kwankwaso da Ganduje ke nufi ga PDP

Kwankwaso ya jinjinawa SuperEagles
AFCON: Kwankwaso ya taya tawagar Najeriya nasarar hayewa mataki na gaba.
Hoto: @KwankwasoRM, @NGSuperEagles
Asali: Twitter

Yadda tawagar Najeriya ta fafata zuwa mataki na gaba

A ranar Litinin, Super Eagles ta lallasa kungiyar kwallon kafa Guinea-Bissau da ci daya mai ban haushi, a wasan karshe na rukunin A wanda ya ba ta damar zuwa wasan zagaye na 16.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kungiyar wacce ke karkashin mai horo Jose Peseiro ta kara da Guinea-Bissau ne bayan fafatawa da kasar Ivory Coast wacce ita ma ta lallasa ta da ci daya mai ban haushi, rahoton Channels TV.

Duk da cewa sun sha matsin lamba a zagayen wasan na farko, sun dawo da karfinsu bayan zuwa hutu, inda dan wasan Guinea-Bissau ya zura kwallo a gidansu a kokari cire ta.

Sakon da Kwankwaso ya aika wa Super Eagles

A halin yanzu dai, Super Eagles za su ci gaba da zama a birnin Abidjan domin karawa ranar Asabar da kungiyar da za ta ci wasan rukunin C, tsakanin Senegal, Guinea ko Kamaru.

Kara karanta wannan

Ba Za Ta Yiwu ba: Dattawan Arewa Sun Yi Tir da Dauke Manyan Ofisoshi Daga Abuja Zuwa Legas

Rabiu Kwankwaso sakon taya murnar da ya aika wa Super Eagles a shafinsa na Twitter ya ce:

“Kun cancanci yabo na tsallakawa zuwa zagaye na gaba. Ku kara kokari don samun nasara a wasannin ku na gaba.”

Karanta sakon a nan kasa:

Karatu da haddar Al-Kur’ani na gyara kwakwalwa – Gwamna AbdulRazaq

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya ba al’ummar Musulmi musamman matasa shawarar mayar da hankali wajen karatu da haddar Al-Kur’ani mai girma.

A cewar Gwamna AbdulRazaq, haddar littafin mai tsarki na gyarawa tare da saita kwakwalwar mai karanta shi.

Asali: Legit.ng





Source link

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here